Majalisar dattawa ta buƙaci Shugabannin tsaron Najeriya su yi Murabus
Majalisar Dattawa a ranar Talata ta buƙaci shugabannin hukumomin tsaro na ƙasar nan su sauka daga muƙamansu saboda cigaba da taɓarɓarewar tsaro a ƙasar.
Majalisar ta cimma wannan matsaya ne bayan Sanata Ali Ndume, (APC, Borno) ya gabatar da ƙudirin nuna damuwarsa kan rahoton murabus ɗin da sojoji fiye da 200 sukayi.
Majalisar ta kuma buƙaci kwamitin ta na tsaro ya binciko dalilin da yasa jami’an sojojin suke yin murabus da kansu.
A jawabinsa, Lawan ya ce duk da cewa Rundunar Sojojin tana iya ƙoƙarin ta don samar da tsaro, ƙoƙarin nata bai wadatar ba.
Ƴan sanda sunyi Ram da masu garkuwa da mutane 33, da ƴan fashi 10
https://www.arewagist.com.ng/2020/07/yan-sanda-sun-damke-gaggan-masu-garkuwa.html?m=1
Akpabio ya yi fallasa, ya bayyana wadanda aka bai wa kwangila
https://www.arewagist.com.ng/2020/07/akpabio-ya-fallasa-waanda-aka-bai-wa.html